Shugaban Jami’ar MAAUN, Farfesa Gwarzo Ya Jajanta Wa Shugaba Bazoum Bisa Rasuwar Surukarsa

MMS HAUSA
0

 


Shugaban Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijer (MAAUN), Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, ya jajanta wa shugaban Jamhuriyar Nijar, Mohamed Bazoum bisa rasuwar surukarsa, Hadjiya Bintou.

Hadjiya Bintou ta rasu ne a ranar 29 ga watan Oktoba, 2022 a birnin Paris na kasar Faransa bayan gajeruwar rashin lafiya.

Farfesa Gwarzo wanda shi ne wanda ya kafa kuma shugaban majalisar gudanarwa na Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya, da kansa ya mika sakon ta’aziyyarsa ga shugaba Mohamed Bazoum a lokacin da ya ziyarci fadar shugaban kasar a Yamai a ranar Laraba 16 ga watan Nuwambar 2022.

Farfesa Gwarzo, har wala yau ya jajantawa shugaban kasar, gwamnati da al’ummar Jamhuriyar Nijar, inda ya bayyana rasuwar Hadjiya Bintou a matsayin babban rashi ba kawai ga danginta kawai ba, har ma ga daukacin al’ummar Jamhuriyar Nijar.

“A madadin iyalina da Jami’ar Maryam Abacha American University (MAAUN), muna mika sakon ta’aziyyarmu ga shugaban kasa Mohamed Bazoum bisa rasuwar mahaifiyarmu, Hadjiya Bintou,” in ji Farfesa Gwarzo.

Ya yi nuni da cewa marigayiyar ta yi rayuwa mai cike da gamsarwa da kuma amfani wanda ya dace a yi koyi da duk wadanda suka kusanci ta a lokacin rayuwarta.

Farfesa Gwarzo, wanda kuma shi ne Shugaban Kungiyar Jami’o’i Masu Zaman Kansu ta Afrika (AAPU), ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki da Ya bai wa Shugaban kasa Mohamed Bazoum da matarsa ​​hakurin jure rashin da ba za a iya mayarwa ba.

Ya kuma roki Allah Madaukakin Sarki da Ya gafarta mata dukkan kurakurenta, ya kuma sanya  marigayiyar a Aljannar Firdausi.

Da yake mayar da bayani, shugaba Mohamed Bazoum ya godewa Farfesa Gwarzo bisa ziyarar ta’aziyyar da ya kai masa, ya kuma yi addu’ar Allah Ta’ala ya saka masa da alheri.

Marigayiya Hadjiya Bintou ita ce mahaifiyar Uwargidan shugaban kasa Mohamed Bazoum, kuma tuni aka binne ta kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar.

Allah ya jikanta da Rahama ya huta lafiya, amin.

Tags

Post a Comment

0 Comments
Post a Comment (0)
To Top