Gaskiyar Yadda Jami’an Tsaro suka afka mana a ranar Muzaharar Kudus A Zariya– ‘Yan Shi’a

MMS HAUSA
0

 


Wakilin almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky a Zariya wadanda aka fi sani da ‘yan shi’a, Shaikh Abdulhamid Bello a hirar da ya yi da manema labarai a Zariya ciki harda wakilin Jaridar MAFITA jim kadan da kammala sallar Idi ta bana a ranar Litinin 2 ga watan Mayun 2022 a makarantarsu ta Fudiyya dake Babban Dodo Zariya, Shehin Malamin ya yi karin haske dangane da abin da ya faru a ranar Kudus a Zariya.

Shehin Malamin ya fara da cewa; “Taron tunawa da ranar Qudus wani taro ne na shekara-shekara wanda musulmin duniya da masu hankali ke nuna goyon bayansu ga al'ummar Palastinu da suke cikin mawuyacin hali a kowacce rana a hannun Sahayoniyawan Haramtacciyar kasar Isra'ila. A bana an gudanar da muzaharorin ne a kusan dukkanin manyan biranen duniya. A Nijeriya an gudanar da muzaharorin ne na lumana a garuruwa sama da hamsin. Babu inda aka kai wa muzaharar hari sai a Kaduna da Zariya wanda ya yi sanadin shahadar mutum daya a Kaduna tare da raunata dimbin ‘yan uwa musulmi maza da mata da harsashi mai rai da jami’an tsaron Nijeriya suka yi. Hakazalika an kama mutane da dama da suka hada da mata da kananan yara, da dama daga cikinsu da raunukan da ke barazana ga rayuwarsu sakamakon harbin da ‘yan sanda suka yi tare da garkame su a hannun ‘yan sanda ba tare da samun kulawar likitoci ba”, ya labarta.

Har wala yau Shehin Malamin ya ce; “muzaharar ta bana a Zariya sun kai mata hari ne bisa makircin cewa muzaharar ta kona ofishin ‘yan sanda na Sabon Gari da wata mota. A tarihin yake cewa an kwashe sama da shekaru arba’in (40) ana gudanar da muzaharorin ranar Kudus a Nijeriya a karkashin jagorancin Shaikh Ibraheem Zakzaky inda a kodayaushe ake tashi lafiya lau har sai dai idan jami’an tsaro ne suka zo suka kawo wa masu muzaharar hari. A don haka abin takaici ne yadda bayan kai harin ga ‘yan kasar da ba su ji ba ba su gani ba, wadanda suke amfani da ‘yancinsu na gudanar da muzaharar lumana, amma kuma har ‘yan sandan za su iya ci gaba da tuhumar masu muzaharar da laifin da wasu ‘yan iska da aka dora wa alhakin tayar da hargitsi suka aikata domin a kama su da laifi tare da tabbatar da kuma tabbatar da munanan laifukan da suka aikata”, ya lurantar.

Shaikh Abdulhamid Bello ya ce; idan dai za a iya tunawa, kimanin watanni ashirin da suka gabata a Kaduna a yayin gudanar da tarukan tunawa da Ashura an dauki jami’an ‘yan sanda a kyamara suna cinna wa motar su wuta, inda ya ce; “wannan wani hali ne da ‘yan sandan Nijeriya suka kware a kai suke kuma yi domin tabbatar da zaluncin da suke yi wa mutanen da ba su ji ba ba su gani ba. Me ya sa jami’an tsaron Nijeriya ba za su karkatar da duk karfinsu da dukiyarsu wajen yakar ‘yan fashin daji da sauran miyagun da suka addabi zaman lafiyar Al’umma ba”, ya tambaya.

Da ya waiwayo kan batun ranar Kudus kuwa, Shehin Malamin ya ce; “Batun ranar Qudus ta duniya ta goyon bayan ‘yan uwanmu Palastinu lamari ne na imani da mutuntaka. A maimakon zama namun daji da nuna rashin wayewa ta hanyar kai hari ga mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, me ya sa gwamnatin Nijeriya ba za ta shirya irin na ta muzaharorin ba na nuna goyon baya ga haramtacciyar kasar Isra'ila da Sahayoniyawan da suka yi kwacen kasar da ba na su ba suke zubar da jinin al'ummar Palastinu da ake zalunta?

“Muna so mu bayyana tare da jaddada cewa ba mu da hannu a cikin kona mota da kuma makircin karya da suke yadawa na kona ofishin ‘yan sanda na Sabon Gari. A don haka muna kira da a gaggauta sakin duk wanda ke hannun ‘yan sanda. Hakazalika muna son mu yi amfani da wannan dama wajen yin kira ga gwamnatin Nijeriya da ta gaggauta sakin takardun fita na Shaikh Zakzaky da mai dakinsa Malama Zeenat domin ba su damar kula da yanayin da suke ciki na rashin lafiya”, ya karkare.

 

 

Tags

Post a Comment

0 Comments
Post a Comment (0)
To Top