Buhari Ya Gana Da Iyalan Waɗanda Suka Rasu Sakamakon Fashewar Sinadarai a Kano

MMS HAUSA
0

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sadu da iyalan da suka rasa rayukansu sakamakon fashewar da aka samu a Kano a makon da ya gabata.

Shugaban wanda ya je Kano domin ƙaddamar da bikin makon rundunar sojin sama ta Najeriya inda rundunar ke cika shekara 58 da kafuwa.

Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa shugaban ya jajanta wa iyalan mutanen da wannan hatsari ya rutsa da su da Sarkin Kano da kuma gwamna kan wannan lamari.
Tags

Post a Comment

0 Comments
Post a Comment (0)
To Top